Kwamitin Shirya Taron Kasa Ya Isa Jihar Barno

Gwamnan Jihar Borno, Kashim Shettima, 8 Agustu 2013

Gwamna Kashim Shettima yayi kira ga kwamitin shirya taron kasa da ya dauki mataki kan wani dan kwamitin kanal Nyiam.
Gwamnan Jihar Borno Hon. K. Shettima yace ya kamata kwamatin sasantawa da jin ba’asi da shugaban kasa ya kafa da ya dauki mataki kan tsohon Kanal Tony Nyam, daya daga cikin Membobin Kwamatin da Gwamnan ya bayyanashi a matsayin dan Juyin mulki.

Gwamna Shattima, ya bayyana haka ne lokacin da yake karbar wakilan Kwamatin karkashin jagorancin dan majalisar dattawa ‘Senata’ Femi Okoromo a fadar Gwamnatin jihar Borno. Yace duk da cewa ‘yan jam’iyyar APC sun bayyana matsayinsu game da wannan taro don haka ba zai yi wata Magana sabanin tasu ba.

Your browser doesn’t support HTML5

Kwamitin Taron Kasa