A na zaman ‘dar’dar a garin ‘Kankara wato hedikwatar mulki ta ‘karamar hukumar ‘Kankara a jihar Katsina, sakamakon fadan daya ‘barke tsakanin fulani da wasu da’ake da’awar ‘yan bangane, lamarin dai yayi sanadiyar akalla rayukan mutane biyar, tare da kona kasuwar garin.