Yanzu haka kungiyoyi da kuma kuma dattawan jihar Taraba na maida martani game da kalaman da gwamnan jihar Taraba Arch. Darius Dickson Isiyaku, na danganta rikicin da aka samu a tsakanin Fulani makiyaya da kuma wasu kabilu a jihar da Boko Haram, batun da suka ce bai dace ba.
A jiya Laraba ma’aikatar Shari’a ta Amurka, ta ce ta nada tsohon shugaban hukumar binciken laifuka ta FBI, Robert Mueller, a matsayin mai bincike na musamman kan yunkurin gwamnatin Rasha na yin katsalandan a zaben shugaban kasar Amurka na shekarar da ta gabata, da kuma wasu batutuwa da suka shafi Rasha.
Gwamnatin Donald Trump ta fitar da sanarwar cewa za ta ci gaba kan tsarin yajejeniyar da ta sassauta takunkumin da aka kakabawa kasar Iran, wanda aka samar tun lokacin mulkin Obama.
Rahotanni na cewa ‘daya daga cikin ‘dalibai ‘yan matan Chibok da kungiyar Boko Haram ta sace shekaru biyu da suka gabata ta kubuta.
Rundunar sojan Najeriya ta Operation Lafiya Dole dake garin Maiduguri, ta ce ta kame wasu mutane 126 da suke zargin cewa ‘yan kungiyar Boko Haram ne, wanda kuma ake zargi da kai hari garin Sabon Gari dake kan hanyar Biu.
Rundunar ‘yan Sandan Najeriya ta fara rangadin ‘kasar domin ganawa da shugabannin al’umma akan matsalar rashin tsaro da ake fama da shi a sassan ‘kasar.
Ratonni da aka wallafa sunce shugaban Amurka Donald Trump ya nemi tsohon shugaban hukumar binciken aikata laifuffuka ta FBI, James Comey, da ya dakatar da binciken da yake gudanarwa kan mai baiwa Trump ‘din shawara kan harkokin tsaron cikin gida Michael Flynn akan dangantakarshi da ‘kasar Rasha, amma fadar white House ta musanta rahotanin.
A jiya Talata ne jakadiyar Amurka a MDD Nikki Haley ta fadawa kasashen duniya cewa, dole ne kasashe su hada kai wajen yunkurin hana kasar da Koriya ta Arewa mallakar makaman Nukiya, tana mai yi musu gargadin zasu iya fuskantar wasu takunkumi idan har suka taimakawa Koriyar wajen samun nasarar shirin ta na Nukiliya.
‘Yan kasashen waje kimanin 335 ne suka sha rantsuwar zama ‘yan Najeriya, duk kuwa da koke-koken da ‘yan kasar ke yi da kuma kushe kasar ta su.
Rahotanni daga jihar Adamawa arewa maso gabashin Najeriya na cewa yanzu hankulan iyaye na tashe sakamakon yawaitar fyaden da ake yiwa kananan yara.
An karfafawa ‘yan jarida gwiwa kan su jajirce wajen gudanar da aikinsu ba tare da fargaba ba.
Noma Tushen Arziki
Babban mashawarcin Amurka kan harkokin tsaron kasa, H.R. McMaster da wadansu jami’an gwamnati shugaba Donald Trump sun musanta sahihancin rahotannin da ke nuni da cewa, shugaban kasar ya gayawa jami’an kasar Rasha wadansu bayanan sirri a ofishinsa dake fadar shugaban kasa.
Amurka ta tasa keyar ‘yan asalin kasar Somaliya dari uku da ishirin da shida zuwa kasarsu, hadi da mutane sittin da bakwai da aka mayar kasar tasu makon da ya shige, abinda ya haura adadin wadanda aka mayar kasarsu a cikin shekara ta dubu biyu da goma sha shida baki daya. Wannan ce shekara ta uku a jere da adadin ‘yan kasar Somaliya da ake maidasu kasarsu ke karuwa.
Hukumar matatar man fetur ta Najariya NNPC, ta ce zata ci gaba da tono ma’adanan Man Fetur da iskar gas a yankin tafkin Chadi da ke jihar Borno.
Rikicin Boko Haram ya yi sanadiyyar karuwar yawan almajirai kan tituna, hakan yasa Jami’ar Amurka da ke Yola a jihar Adamawa, ta sake kaddamar da shirinta na koyar da ciyar da almajirai a karo na biyu.
Kimanin wata daya da kafofin yada labarai a Najeriya suka ba da labarin kakaki majalisar jihar Adamawa Kabiru Mijinyawa, ya yi wa sajen Umaru Dan sanda mai tsaron lafiyarsa duka, lamarin da rundunar yan sandan ta ce tana gudanar da bincike a kai.
Wata kungiyar yan bindiga a Ivory Coast ta kaddamar da wani hari don kwato yankin birnin tsakiyar kasar na Bouake daga sojojin gwamnati bisa bukatar cika musu alkawarin karin kudi.
Kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya yana shirin gudanar da wani taron gaggawa a gobe Talata a kan gwajin makami mai lizzami da Korea ta Arewa na baya bayan nan.
Domin Kari