Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Adadin Wadanda Suka Mutu Da Cutar Ebola A Kasar Kwango Ya Karu


Wani fada ya ziyarci cibiyar jinyar masu cutar Ebola
Wani fada ya ziyarci cibiyar jinyar masu cutar Ebola

An sake samun wani da ya mutu da cutar Ebola a Congo, abinda ya kai adadin wadanda cutar ta kashe zuwa goma sha biyu, bisa ga cewar ma’aikatar lafiya ta Damokaradiyar Jamhuriyar Kwango.

Rasuwar ta auku ne a kauyen Iboko dake arewa maso yammacin lardin Equater.

Ma’aikatar lafiya tace akwai kuma wadansu mutane hudu da ake kyautata zaton sun kamu da cutar a lardin. Yanzu haka an tabbatar mutane talatin da biyar sun kamu da cutar ta Ebola a kasar Kwango.

Gobe litinin za a fara allurer rigakafin cutar Ebola a kauyukan Bikoro da Iboko dake lardin Equateur. Ana kuma shirin rigakafi a Mbandaka, babban birnin lardin mai mutane miliyan daya da dubu dari biyu, dake bakin kogin Kwango, inda aka tabbatar da mutane hudu sun kamu da cutar.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG