Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An fara rajistar masu zabe yau a Najeriya


Shugaban Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, (INEC) Attahiru Jega yana nuna jadawalin zaben shekara ta 2011 (File Photo).
Shugaban Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, (INEC) Attahiru Jega yana nuna jadawalin zaben shekara ta 2011 (File Photo).

Yau hukumar zabe ta Najariya ta fara rajistar masu zabe a duk fadin kasar.

Yau hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya watau INEC ta fara aikin rajistar masu zabe, wanda zai basu damar samun katin kada kuria a zabukan da za a gudanar kwatar farko wannan shekarar. Sai dai duk da tabbacin da hukumar zaben ta bayar cewa ba za a sami matsala ba, rahotanni na nuni da cewa, an fara gudanar da aikin a makare a cibiyoyi da dama. Bisa ga rahotannin, wadansu jami'an rajistar sun fuskanci matsalar amfani da na'urar. Hukumar zabe mai zaman kanta zata dauki makonni biyu tana aikin rajistar

XS
SM
MD
LG