Wani sabon hari da aka kai a karamar hukumar Logo da ke jihar Benue ya tarwatsa dubban mutanen yankin da dama wadanda suka fantsama zuwa jihar Nasarawa da ke makwabtaka da jihar.
Akalla mutane 16 ne suka rasa rayukansu, ciki har da wani basaraken gargajiya a cewar rahotanni.
Wata rubutacciyar sanarwa da jami’an tsaron jihar suka fitar ta nuna cewa mutum 10 ne suka rasu.
Hukumar ba da agajin gaggawa a jihar Nasarawa ta tabbatar da kwararar dubban ‘yan gudun hijra zuwa yankin jihar.
“Adadinsu ya kai kusan dubu 16, yanzun nan suna warwatse a kananan hukumomi biyu, wato Keana da Awe.” Inji shugaban hukumar ba da agaji a Nasarawa, Barrister Zakari Ali Maga.
Harin na zuwa ne kasa da mako guda bayan wani mummunan hari da aka kai a wasu kananan hukumomin jihar ta Benue, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 50 kamar yadda rahotanni ke nunawa.
Jihar ta Benue ta sha fama da rikice-rikicen da ake dangantawa da rashin jituwar makiyaya da manoma.
A baya, gwamnatin jihar ta kafa dokar hana kiwo a warwatse, lamarin da ya sha suka daga makiyaya.
Saurari rahoton wakiliyar Muryar Amurka, Zainab Babaji:
Facebook Forum