Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kaiwai Wasu Sarakuna Farmaki


Marigayi sarkin Gwoza Alhaji Shehu Idris Timta da 'Yan Boko Haram suka kashe.
Marigayi sarkin Gwoza Alhaji Shehu Idris Timta da 'Yan Boko Haram suka kashe.

‘Yan Boko Haram sun kashe sarkin Gwoza.

‘Yan Boko Haram sun kai wani farmaki kan ayarin wasu sarakuna a tsakanin garuruwan Zur, da shaffa ciki

n jihar Borno akan hanyarsu ta zuwa wajen janaizar Sarkin Gombe Alhaji Shehu Abubakar.

Kamar yanda rahotani ke nunawa ‘yan bindigan wadanda sun fi dari sunyi kwanton bauna ne akan hanyar Zur da Shaffa, a jihar Borno.

Inda nan take suka budewa motocin sarakuna wuta da bindigogi, sarakuna da abun ya ritsa dasu, sun hada da Sarkin Uba, Ismaila Mamza da kuma sarkin Gwoza Idris Timta.

Wannan farmakin yayi sanadiyar rasuwar sarkin Gwoza Idris Timta, shidai Sarkin na Gwoza ana haifar ne a shekaran 1948, ya kuma samu ilimisa a Jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria.
please wait

No media source currently available

0:00 0:01:34 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG