Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Buhari Na Jimamin Rasuwar Dr. Ibrahim Datti Ahmed


Marigayi Datti Ahmed

Wani dattijo kuma Shugaban Majalisar Koli ta Shari'a a Najeriya (SCSN), Dr Datti Ibrahim Ahmed, ya rasu.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nuna juyayi bisa rasuwar tsohon shugaban majalisar koli ta shari'a a Najeriya, Dr. Ibrahim Datti Ahmed.

Shugaban kasar a cikin ta'aziyyar tunawa da marigayin wanda likita kuma dan siyasa wanda ya taba tsayawa takarar shugaban kasa, ya bayyana tsohon shugaban majalisar koli ta shari'an Najeriya a matsayin n mutum mai albarka da tarin hikima.

Hakan ya fito ne a wata sanarwa da kakakin shugaba Buhari, Malam Garba Shehu ya fitar.

Marigayi Datti ya rasu da sanyin safiyar Alhamis a jihar Kano. Shekarunsa 83.

Dr. Datti ya taba tsayawa takarar shugaban kasa.

Marigayi Ahmed ya rasu ya bar mata daya da ‘ya’ya 10. Tuni aka yi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG