Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dubun Wasu Masu Safarar Miyagun Kwayoyi Ta Cika a Nijer


Hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi a jamhuriyar Nijer ta kama wasu mutane kimanin 10 wadanda ta ce dubunsu ta cika ne a lokacin da suke kokarin shiga birnin Yamai da lodin kwalayen kwayar Tramadol da suke kokarin shigarwa a kasuwannin kasar ta Nijer da wasu kasashen yankin Maghreb.

Wasu bayanai da suka shigowa ‘yan sanda a farkon watan nan na Janairu ne suka sanya hukumar OCRITIS mai yaki da fataucin miyagun kwaoyoyi ta kasar kaddamar da bincike wanda a karshe ya bada damar gano rukuni na farko na wasu ‘yan Nijer 3 dauke da kwayar Tramadol kimanin 4,000, wadanda suka fito da su daga jihar Kano da ke arewacin Najeriya

Masu Safarar Miyagun Kwayoyi a Nijar
Masu Safarar Miyagun Kwayoyi a Nijar

Sai rukuni na biyu na wasu mutane 7, su ma ‘yan Nijer ne da suka fito daga kasar Togo dauke da kwayar Tramadol sama da 100,000, kamar yadda mai magana da yawun hukumar ‘yan sandan Nijer Kwamishiniya Nana Aichatou Ousmane Bako ta yi wa manema labarai bayani a lokacin da aka gabatar da wadannan mutane.

Binciken ya yi nuni da cewa, gagarumin yaki da masu safarar miyagun kwayoyin da aka kaddamar a Jamhuriyar Nijer da makwafta ya haddasa karancin kwayar Tramadol a kasuwanni, lamarin da kuma ya janyo tsadarta a yanzu haka, shi ya sa suka fara neman hanyoyin samo kwayar ta Tramadol ruwa a jallo, inji mataimakiyar babban Alkali mai kare muradan hukumar Procureur de la Republique, Mme Maidamma Hadiza.

Miyagun kwayoyi a Nijar
Miyagun kwayoyi a Nijar

A ci gaba da karfafa matakan yaki da fatauci da shan miyagun kwayoyi, hukumar OCRTIS ta bude layin waya na musamman wanda jama’a za su iya kira don tsegunta wa jami’anta dukkan wani abinda ake zargin ya na da alaka ko ta’ammali da miyagun kwayoyi.

Hukumar ta OCRTIS ta kuma gargadi iyaye su kara maida hankali wajen tantance yanayin mutanen da ‘yayansu ke hulda da su a matsayin abokai ko kawaye.

Saurari cikakken rahoton Souley Moumouni Barma:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:03 0:00


Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG