Gobarar ta tashi ne a cikin wani otal mai suna Arpit Palace a wani bangare mai cike da jama’a a tsakiyar birnin Delhi, inda hotuna suka nuna yanda wutar take cinye ginin.
Mun tabbatar da wannan labarin tare da hukumomin asibitoci, da suka fada mana mutane 17 uka mutu ciki har da karamin yaro, inji Sunil Choudhary wani jami’in ‘yan kwana-kwana yana fadawa kamfanin dillancin labarai na AFP
Wasu kafafen labarai na cikin gida sun ce wata mace da danta sun mutu ne yayin da suka yi kokarin tserewa wutar suka tsallako a cikin taga.
Facebook Forum