Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jam'iyyun Siyasa A Afrika Ta Kudu Sun Kimtsa Shiga Zabe Gobe Laraba


Shugaban Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa

Gobe Laraba al’ummar Afrika ta Kudu zasu kada kuria’a a zaben da ka iya zama kalubala mafi girma da jam’iyar ANC mai mulki zata fuskanta. Yayin da jam’iyar da abokan hamayyarta suke kokarin jawo ra’ayin masu kada kuri’a da basu yanke shawara kan jam’iyar da zasu zaba ba.

Jam’iyar ANC da Democratic Alliance da kuma sabon tashe jam’iya mai hankoron farfado da tattalin arziki Economic Freedom Fighters sun yi gangamin yakin neman zaben su na karshe a Johannesburg babban birnin kasuwancin kasar.

Jam’iyar ANC tana kan gaba da sauran jam’iyu 48 da suka tsaya takara, sai dai jam’iyar dake mulkin kasar tun shekarar alib da dari tara da casa’in da hudu tana fuskantar suka kan batun cin hanci da rashawa. Shugaban jam’iyar, kuma shugaban kasar Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa ya amince da haka a jawabinsa ranar Asabar.

Ramaphosa yace sun amince da cewa sun tafka kurakurai, kana yace sun kuma zo gaban al’ummar su saboda sun yarda da kasawar su, yace sai dai wadanda basu yin komi ne kawai basu kuskure.

Bisa ga cewar hukumar zabe, ‘yan Afrika ta Kudu miliyan ishirin da shida da dubu dari bakwai ne suka yi rajistar kada kuri’a a zaben da za a gudanar gobe Laraba.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG