Babban sakataren MDD yace ya tabbatar da Mr. Haysom nada kwarewa kuma mutum ne mai daraja wanda ya yi aikin hukuma a matsayin kasa da kasa, wanda kuma ya taka rawar gani a shugabanci a wurare da dama da ma helkwatan MDD, inji mai magana da yawun Antonio Guterres a jiya Juma’a. Sai dai babban sakataren yace har yanzu zai ci gaba da bada himma a kan bukatun mutanen Somalia a cikin ayyuakan da Majalisar keyi a Somalia.
Gwmnatin Somalia ta ayyana babban wakilin MDD Haysom a matsayin wanda bata kaunarsa a cikin kasar tun ranar farkon wata Janiru kuma ta umarce shi da bar kasar bayan watanni hudu kacal da ya fara aiki a matsayin wakilin babban sakataren MDD na musamma kuma ya shugabanci ofishin Majalisar a wannan kasa.
Gwamnatin ta nuna fushinta a kan wata wasika da Haysom ya aikewa hukumomin kasar inda ya tado da batun tsohon shugaban kungiyar al-Shabab Mukhtar Robow wanda ya shiga siyasa kuma ya bayyna aniyarsa ta shiga takarar zabe da za a gudanar a yankin kudu maso yammacin kasar.
Facebook Forum