WASHINGTON, DC —
Wasu gwamnatoci da kungiyoyi har ma da daidaikun mutane na ci gaba da kokarin kwakulo hanyoyin da suke ganin za a iya bi a magance rigingimun da ke yiwa ci gaban rayuwa barazana a kasar Najeriya.
Daya daga cikin irin wadannan gwamnatoci ita ce gwamnatin jahar Kaduna wadda ta yi amanna cewa babban taron da ake shirin yi a cikin watan nuwamba na manyan biranen duniya da suka taba fama da tashe-tashen hankula da rigingimu amma suka samu hanyoyin ganin bayan su, zai taimaka matuka wajen samar da zaman lafiya mai dorewa.
Wakilin Sashen Hausa a jahar Kaduna Isah Lawal Ikara ya na da karin bayani a cikin wannan rahoto.
Daya daga cikin irin wadannan gwamnatoci ita ce gwamnatin jahar Kaduna wadda ta yi amanna cewa babban taron da ake shirin yi a cikin watan nuwamba na manyan biranen duniya da suka taba fama da tashe-tashen hankula da rigingimu amma suka samu hanyoyin ganin bayan su, zai taimaka matuka wajen samar da zaman lafiya mai dorewa.
Wakilin Sashen Hausa a jahar Kaduna Isah Lawal Ikara ya na da karin bayani a cikin wannan rahoto.