Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rajistan 'Ya'yan APC a Bauchi da Gombe ya sa Wasu Yin Korafi


APC
APC

A cigaba da yiwa 'ya'yanta ragista jam'iyyar APC ta gamu da nasara da kuma matsaloli a Bauchi da Gombe

Rahotanni na nu cewa aikin rajistan da jam'iyyar APC ke yi a duk fadin Najeriya ya samu nasarori da kuma matsaloli.

Injiniya Abubakar Abdullahi shi ne wanda jam'iyyar APC ta tura zuwa jihar Bauchi domin ya shugabanci kwamitin yin rajistan. Ya ce sun samu matsalar wasu kayan aiki wanda ya sa dole suka tafi Jos da Kano kafin su samu wasu dalili ke nan ranaku biyu na farkon soma rajistan sun tafiyar hawainiya. Amma daga bisani ayyuka sun cigaba ba tare da wata matsala ba.

Amma a jihar Gombe dan majalisar wakilai Ahmed Maitantarki ya ce an yi aikin yin ragistan ba bisa kaida ba. Ya ce an yi abubuwa da yawa da basu kan kaida. Kafin a fara yin rajista ya ce su mika kukansu ga uwar jam'iyya domin tsarin da aka tanada bai zo daidai da abun da jam'iyyar ta tsayar ba. Ya ce kaidar da aka yi anfani da shi basu yadda da shi ba. Ya ce sun yi taro da shugabanninsu daga kananan hukumomi har jiha suna kiran uwar jam'iyya ta yi gyara.

Amma Sanato Gwamni Zanna Boma shugaban kwamitin yin rajistan a jihar Gombe ya ce bashi da masaniya kan korafin da Ahmed Mailantarki ya yi. Ya ce idan akwai koke to zai kaiwa uwar jam'iyyar. Sai dai jogo a jam'iyyar Usman Bayero Nafada ya shawarci masu sha'awar tsayawa takara. Ya ce idan jam'iyya tana da farin jini dole ne a samu 'yan takara da yawa. Sabili da haka bayan an kammala rajista ya kamata a zauna a daidaita.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:59 0:00
Shiga Kai Tsaye
Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG