Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Buhari Ya Rantsar Da Olukayode Ariwoola A Matsayin Mukaddashin Alkalin Alkalan Najeriya


Tambarin Kotun kolin Najeriya
Tambarin Kotun kolin Najeriya

Mai shari’a Olukayode Ariwoola ya sha rantsuwar kama aikin maye gurbin Tanko Muhammad wanda ya yi murabus da safiyar Litinin, bisa dalilan rashin lafiya.

ABUJA, NIGERIA - Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya rantsar da Olukayode Ariwoola a matsayin sabon alkalin alkalan kasar na riko ‘yan sa'o'i bayan da tsohon babban mai shari’a Tanko Muhammed ya yi murabus.

A wajen bikin rantsuwar, shugaba Buhari ya fadi cewa ya samu wasikar murabus din Tanko Muhammed ranar Litinin, wanda dama ya kamata ya yi ritaya daga kotun kolin a karshen shekarar 2023.

A shekarun aluf dari tara da sittin ne dai aka haifi Ariwoola, ranar 22 ga watan Agusta a garin Oluwoye da ke karamar hukumar Iseyin a jihar Oyo inda kuma ya yi karatun firamare a makarantar gwamnati ta demonstration da ke garin tsakanin shekarar 1959 zuwa 1967.

Ya yi karatun gaba da firamare a makarantar Muslim Modern School ta garin nasu a tsakanin shekarar 1968 zuwa 1969 kafin ya wuce makarantar Ansar-Ud-Deen da ke garin Saki na karamar hukumnar Oyo ta arewa.

Ariwoola ya fara aiki a matsayin mai ba da shawara kan harkokin bautar kasa wato NYSC na jiha a ma’aikatar shari’a ta birnin Akure a jihar Ondo sannan ya zama jami’in shari’a a ma’aikatar shari’a ta jihar Oyo har zuwa shekarar 1988 inda a kashin kansa ya bar aikin gwamnati don bude kamfanın shari’a na kansa.

Mai shari’a Ariwoola ya yi aiki a matsayin Lauya a ofishin aikin lauya Cif Ladosu Ladapo mai mukamın SAN tsakanin watan Oktoban shekarar 1988 zuwa Yulin 1989 lokacin da ya kafa nasa ofishin mai suna Olukayode Ariwoola & Co - kamfanin lauya da masu ba da shawara a garin Oyo a watan Agustan shekarar 1989, daga nan kuma aka nada shi a watan Nuwamban shekarar 1992 a matsayin Alkalin Alkalan Jihar Oyo.

Hakazalika, mai shari’a Ariwoola ya taba zama Alkalin Kotun daukaka kara ta Najeriya, kuma a ranar 22 ga Nuwamba shekarar 2011 aka nada shi a matsayin alkalin kotun kolin Najeriya, wanda tsohon babban jojin Najeriya ya rantsar da shi.

A yanzu dai mukaddashin alkalin alkalan Najeriya da shugaba Buhari ya nada na jiran amincewar majalisar dattawan Najeriya bayan murabus din Mai Shari’a Tanko Muhammad.

A ranar 25 ga watan Janairun shekarar 2019 ne shugaba Buhari ya rantsar da tsohon babban alkalin alkalan kasar, mai sharia Tanko Muhammad wanda ya yi murabus.

XS
SM
MD
LG