Bayan yarjejeniyar afuwar kuma, Assad da ministan tsaron Rasha Sergei Shoigu sun ce gwamnatocin Rasha da Siriyya zasu bude wasu hanyoyin fita birnin Aleppo guda 3 don fararen hula da yan tawayen da suka amince su ajiye makamansu, sai kuma hanya daya don yan tawayen da basu amince ba kuma suna so su gudu da makamansu.
A wani jawabi da suka yi ta kafar Talabijin, Shoigu da shugaba Vladimir Putin sun ce nan ba da jimawa ba zasu fara aikin bada agaji mai yawan gaske a wajen Aleppo don taimakawa fararen hular da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su, har ma da mayakan suka yarda su ajiye makamansu.
Bayan hanyoyin da za a bude kuma, Shoigu ya fadi cewa zasu tanadar da sansanonin bada abinci, da magunguna a wajen birnin.