Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu Kungiyoyi Masu Zaman Kansu A Najeriya Suna Bada Kyautar Hannu Da Kafar Roba


Kungiyar Izalatul Bidia waikamatus sunna (JIBWIS) da hadin gwiwar wata kungiyar da ake kira TOLORAM daga kasar India suna bada kyautar hannu da kafar roba kyauta a Abuja

Kungiyar Izalatul Bidia Waikamatus Sunna (JIBWIS) da hadin kan wata kungiyar kasar India mai suna TOLORAM,suka taimakawa wasu bayin ALLAH masu laluran rashin hannu ko kafa.

Mutane kusan dubu biyu ne wadannan kungiyoyin zasu baiwa hannu ko kafan roba kyauta, wanda aka kiyasta kudin sa a Najeriya yakai naira dubu dari biya kowane guda.

Yayin da kungiyar JIBWIS, ke daukar dawainiyar masu wannan lalurar daga ko ina cikin Najeriya zuwa Abuja kuma su basu wurin kwana da ciyarwa, ita ko kungiyar ta TOLORAM ta kera kafa ko hannu kyauta.

Kungiyar tace duk wani mai wannan lalurar ya tafi ofishin kungiyar ta JIBWIS domin yayi rajista, sabo da samunwannan kyautar.

Malam Usman Funtua dake kula da aikin a madadin kungiyar ta JIBWIS yace tallafin bai tsaya ga musulmi kawai ba ko kuma wata darika ko kungiya ba, duk wanfda yazo za a bashi kyauta.

Ga Nasir Adamu El-Hikaya da Karin bayani.2’54

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:54 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG