George Bizos, Lauyan Da Ya Kare Nelson Mandela Ya Rasu

George Bizos

Kasar Afrika ta Kudu na alhinjn mutuwar dan gwagwarmayar yaki da wariyar launin fata baban Lauya George Bizos, wanda ya yi suna wajen kare tsohon shugaban kasar marigayi Nelson Mandela.

A cewar iyalan Bizos ranar Alhamis 10 ga watan Satunba, marigayin wanda aka haifa a kasar Girka, ya je Afrika ta Kudu ne a matsayin dan gudun hijira a lokacin yakin duniya na 2, ya rasu a jiya Laraba a gidansa yana da shekaru 92 a duniya.

A wani jawabi da Shugaban Afrika ta Kudu Cyral Ramaposa ya yi, ya bayyana margayi Bizos a matsayin “Mikiyar kasar ta fannin shari'a."