Fitaccen lauyan nan mai rajin kare hakkin bil’adama, Femi Falana, ya yi kira da a dawo da zunzurutun kudadden da tsohon gwamnan jihar Delta, James Ibori ya wawure ya kai kasar waje da suka kai fam milyan 4 da dubu 200 ruwa, cikin lalitar gwamnatin yankin Naija Delta.