Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Batare Da Bata Lokaci Ba Za a Sake Gina Garin: Hassan Rouhani


Biyo bayan girgizar kasar da ya hallaka mutane da dama da kuma jikkata wasu gwamnatin kasar Iran ta ayyana yau a zaman ranar makoki a kasar.

A yau talata, shugaban kasar Iran Hassan Rouhani, ya dauki alkawarin cewar gwamnatin sa ba tareda wani bata lokaci ba, zata sake gine wuraren da mummunar girgizar-kasa ta shafa, a yayin da kasar ta ayyana yau a zaman ranar makoki.

Rouhani yayi magana ne a lokacin da ya kai ziyara yankin Kermanshah inda bala’in yafi yin barna a girgizar mai karfin awo 7.3, a ma’aunin mutsin kasa daya afkawa yankin ranar Lahadi, akan iyakar Iran da Iraqi.

kafar yada labaran kasar Iran ta sanar da cewa a kalla mutane 530 ne suka rasa rayukan su kuma mutane 7000 suka ji rauni.

Mafi yawancin wadanda abin ya shafa mazauna Sarpol-e-Zahab ne dake lardin Kermanshah. Sai dai makwabciyarta Iraqi kuma, ma'aikatar cikin gidan kasar ta bayyana cewa mutane bakwai ne suka rasu kuma 500 suka jikkata.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG