Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ra'ayoyin 'Yan Najeriya Sun Banbanta Kan Cire Kasar daga Jerin Kasashe Masu Tauye 'Yancin Addini


Sakataren gwamnatin Amurka Anthony Blinken da Ministar Harkokin Wajen Najeriya Geoffrey Onyeama
Sakataren gwamnatin Amurka Anthony Blinken da Ministar Harkokin Wajen Najeriya Geoffrey Onyeama

Daya daga cikin bayanan da Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Anthony Blinken yayi a ziyarar da ya kai Najeriya shi ne albishir da ya yi wa kasar na cire sunanta daga jerin kasashen da ke tauye 'yancin addini, batun da ya dauki hankalin al'umma.

A shekara 2020 ne Amurka ta ayyana Najeriya a matsayin kasa da ke tauye yancin mabiya addinai daban daban da ake da su a kasar, amma da wannan jawabin na Anthony Blinken, yanzu Najeriya ta fice daga cikin jerin kasashen da aka hada a wannan shekara ta 2021.

Shugaban gudanarwa ta Kungiyar Amnesty International Auwal Musa Rafsanjani yana ganin wannan mataki da Amurka ta dauka ya yi daidai domin tun dama ba mutane da dama ba su goyi bayan cewa Najeriya kasa ce da ke tauye ýancin addini ba domin kowa da ke kasar yana irin bautar da yake so ne.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Anthony Blinken da Shugaban Najeriya Muhammadu Buha
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Anthony Blinken da Shugaban Najeriya Muhammadu Buha

Rafsanjani ya ce gwamnati bata taba sa baki a yadda mutanen kasar ke addinin su ba, sai dai wasu 'yan kasa ne kawai suka zuga Amurka a lokacin da ta sa Najeriya a ayarin masu tauye 'yancin addini.

Shi kuwa Malamin Tsangayar siyasa da diflomasiyar kasa da kasa a Jamiár Abuja Dokta Bibi Farouk yana ganin za a iya kalon wannan mataki da kasar Amurka ta dauka ta fanoni uku, kuma wanda yake da inganci shi ne cewa Najeriya tayi aiki sosai ta fanin diflomasiya, kuma ta nuna cewa irin wannan batu abune da ake yi a bayan fage ba a bayyane ba. Bibi ya ce abu na biyu shine cewa an yi bincike an gano kowa yana addinin da ya so ne a Najeriya, babu wanda yake tsangwaman wani saboda addinin sa. Abu na uku kuma ,tsarin tafiyar da diflomasiya a kasa, akwai yarda cewa abubuwa da ke faruwa a cikin gida suna da tasiri akan yadda kasar take tafiyar da harkokin ta na waje.

sababbin-kudurorin-amurka-kan-nahiyar-afirka

ziyarar-sakataren-gwamnatin-amurka-anthony-blinken-a-najeriya

gwamnatin-najeriya-na-dakon-rahoton-gwamnoni-kafin-ta-dauki-mataki-kan-batun-endsars

Sakataren gwamnatin Amurka Anthony Blinken da Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo
Sakataren gwamnatin Amurka Anthony Blinken da Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo

Amma ga babban mukarabbin mallam ibrahim Elzakzaki na kungiyar shiá Mohammed Ibrahim Gamawa yana ganin ba a yi wa yan Shiá adalci ba, saboda Amurka tana gani aka yi wa ýaýan kungiyar kisan mumuke amma yanzu sai ta fito ta ce ta wanke Najeriya da sabulun salo? Gamawa ya ce akwai abin dubawa.

A ayarin kasashen da ke tauye yancin addini na shekara 2021 akwai kasashe 10 ciki har da kasar China da Rasha. Anthony Blinken ya ce gwamnatin Amurka za ta cigaba da saka takunkumi kan kasashe da gwamnatocin ke hana yan kasar yin addinin da suke so.

Saurari cikakken rahoton Madina Dauda cikin sauti:

Ra'ayin 'Yan Najeriya Kan Cire Kasar a Jerin Kasashe Masu Tauye 'Yancin Addini-3:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:16 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG