Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Trump Ya Jinjinawa Ma'aikatan Amurka


APTOPIX Trump
APTOPIX Trump

Sai dai izuwa yanzu babu wani ci gaba da aka samu a kokarin kawo karshen rufe ma’aikatun da ya shiga kwana na talatin da biyu yau.

Trump ya sake jadada kira da a gina katanga kan iyakar Amurka da Mexico a sakonsa na twitter inda yace, “tilas ne muyi aiki tare yanzu, bayan shafe shekaru ana watsi da batun, mu kawo karshen matsalar bukatun jinkai, da masu aikata miyagun laifuka a kan iyakarmu. Zamu yi gagarumar nasara.

A makon nan, Trump ya yi wani tayi da nufin bude ma’aikatun gwanatin inda yace zai bada izini zama Amurka na tsawon shekaru uku ga daruruwan ‘yan gudun hijiran da iyayensu bakin haure suka shigo da su Amurka suna kanana da ake kira DREAMERS, idan zai sami dala miliyan dubu biyar da dari bakwai da yake bukata na gina katanga, da nufin shawo kan matsalar bakin haure.

‘Yan Jam’iyar Democrat dai sun ce akai kasuwa.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG