Yajin aikin gargadi na kwanaki uku da ma'aikatan hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya wato NRC suka yi ya hana zirga-zirgar jiragen kasa a fadin kasar.
Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi garkuwa da akalla mutane biyar a wani kamfanin ruwan leda a garin Tegina da ke karamar hukumar Rafi na jihar Naija.
Akalla ma’aikatan hukumar ICPC 50 ne suka bayyana a gaban wani kwamitin hukumar kan tantance takardun shaidar karatu da bayanan hidima inda aka gano wasu kura-kurai a shekarun su da kuma takardun shaidarsu na kammala karatu.
Ministan shari’a kuma antoni janar na tarayyar Najeriya, Abubakar Malami, ya sake nesanta kansa da ofishin antoni janar daga madugun wadanda ake zargi da hannu a kutsen da aka kai gidan alkaliyar kotun koli mai shari’a Mary Odili.
Ministar kudi, kasafi da tsare-tsare ta kasa, Zainab Shamsuna Ahmed, ta bayyana cewa fasakwauri ne ke haddasa tashin farashin shinkafa a Najeriya.
Rahotanni daga jihar Borno sun yi nuni da cewa akasarin ‘yan gudun hijirar da ke zama a sansanin Bakassi sun bayyana aniyarsu ta komawa gida da kuma komawa gudanar da ayyukan noma domin samun abin dogaro da kai maimakon dogaro da dan kankanin kayan agaji da ake ba su.
Rundunar yan sandan Najeriya ta sami nasarar kama mutane 14 da ake zargin suna da hannu a kutsen da aka kai gidan babbar jojin kotun koli, mai shari’a Mary Odili, da ke birnin Abuja a ranar Alhamis.
Dage sauraron shari’ar Nnamdi Kanu na zuwa ne bayan tawagar lauyoyinsa sun gudanar da wani tattaki kan matakin da jami’an hukumar tsaro ta DSS suka dauka na hana wasu daga cikin lauyoyinsa damar shiga cikin kotun.
Wani kwamitin bincike da kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya wato ASUU ta kafa a jami’ar fasahar Owerri ta jihar Imo, ya ce an bi tsarin da ya dace wajen bai wa dakta Isa Ali Pantami matsayin farfesa a fannin dabarun tsare yan kasa a yanar gizo.
Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu ya bayyana cewa Najeriya za ta kwashe tsawon shekaru 120 kafin ta kai ga samun wadatattun likitocin da ake bukata a fannin kiwon lafiya, kuma sai idan likitocin sun ci gaba da zama a kasar ba tare da ficewa ba.
Hukumar zabe ta Najeriya mai zaman kanta wato INEC ta dakatar da aikin tattara sakamakon zaben jihar Anambra da aka fara gudanarwa a ranar asabar inda ta ayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba.
Tawagar hadin gwiwa ta jami’an tsaro a jihar Ekiti ta sami nasarar kashe wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne a wurin karbar kudin fansa a wani dajin da ke tsakanin iyakar jihohin Ekiti da Kwara.
Rundunar ‘yan sandan birnin Abuja ta tabbatar da ceto mutane 6 ciki har da malamai biyu da aka sace daga jami’ar birnin tarayya Abuja da aka fi sani da UNIABUJA.
'Yan takara 13 a zaben gwamnan jihar Anambra da ke gabatowa sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a Awka, babban birnin jihar.
Rundunar sojin Najeriya ta sami nasarar halaka sama da ‘yan ta’adda 30 bayan wani samame da dakarun hadin gwiwa wato OPHK suka kai a wata maboyan ‘yan ta’addar a jihar Borno da ke yankin arewa maso Gabas.
Gwamnan Nyesom Wike na jihar Ribas, ya bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga gwamnatin tarayyar Najeriya da ta yi binicke kan wadanda suka kutsa kai cikin gidan mai shari’a Mary Odili.
Matasa a jihar filato sun yi tattaki zuwa majalisar dokokin jihar Filato domin nuna bacın ransu kan tsige matashi dan uwansu wato kakakin majalisar, Abok Ayuba Nuhu da 'yan majalisar suka yi.
Rahotanni daga jihar Taraba sun yi nuni da cewa wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa ne sun rasa rayukansu a wani fadan raba kudin fansa da suka yi a tsakaninsu.
Mazauanan garin Damboa na ci gaba da tserewa don neman mafaka a garuruwa makwabta sakamakon harin da wasu mahara da ake zargin mambobin kungiyar Boko Haram ne suka kai a garin da maraicen ranar Alhamis.
Hamdok, masanin tattalin arziki ne da ya taba aiki da Majalisar Dinkin Duniya. An zabe shi a matsayin Firai minista na wucin gadi a watan Agustan 2019.
Domin Kari