Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Yiwa Sojoji Kwanton Bauna a Adamawa


Mayakan Ruwa suna hallartar taron sauyin shugabanci a birnin Abuja Junairu 20, 2014.
Mayakan Ruwa suna hallartar taron sauyin shugabanci a birnin Abuja Junairu 20, 2014.

Wasu ‘yan bindiga sunyi wa sojojin Najeriya kwanton bauna a karamar hukumar Madagali dake jihar Adamawa.

Tuni wasu al-ummomi dake kunshi da mutane fiye da dubu a yankin suka kauracewa gidajensu zuwa shedkwatar karamar hukumar, yayinda har yanzu ba’a san inda wasu suka shiga ba.

Wannan dai na zuwa ne yayinda ake cigaba da jimamin kwanton baunan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa sojoji a yankin Izge, yayin da sojojin ke kan hanyar kai ceto.

Da yake tabbatar da halin da al-umman kan iyakar ke ciki da kuma kwanton baunan da aka yi wa sojojin, daya daga cikin shuwagabannin karamar hukumar Madagali, Mr. Maina Uluramo yace ‘yan bindiga sun tarwatsa al-ummomi da dama, saboda haka ne suke kiran a kafa rundunana musamman a yankin.

Mr. Maina yace “an kawo zuwa Izge, to su kuma mutanen Izge suna guduwa zuwa Madagali. Muna kiran gwamnati ta dauki mataki akan wannan abun, a san yanda za’a yi tsare wannan waje inda mutane suke”.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:10 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG