A yayin da hare-haren ‘yan bindiga suke kara uzzura a jihar Zamfara da ke Arewacin Najeriya, rundunar sojin saman kasar ta ce ta kai wani mummunan hari ta jiragen sama, wanda yayi sanadiyyar hallaka ‘yan bindiga kusan 100, da kuma wargaza sansanoninsu kusan 7 a jihar.