A cigaba da barna da kungiyar Al-Shabab ke yi a Somaliya da kewaye, wannan mugunyar kungiyar ta sake kashe mutane a kalla 15 kuma da alamar adadin mace-macen zai iya karuwa.
A cigaba da fadawa cikin hatsari da 'yan gudun hijira ke yi a sassan duniya, wasu 'yan kudun hijira, wadanda ba a tantance kasashen da su fito ba, sun hallaka wani hatsarin mota.
A wani al'amari mai ban al'ajibi, rahotanni na nuna cewa dan jarida Jamal Khashoogi ya kunna na'urar daukar sauti da bidiyon agogonsa kafin ya shiga ofishin jakadancin Saudiyya da ke Turkiyya, inda ake tsammanin an kashe shi.
A wani al'amari mai karkada hanji, mugunyar cutar nan ta Ebola ta kama wani ma'aikacin Majalisar Dinkin Duniya a Kongo. Rahotanni na nuna cewa cutar na dada yaduwa.
Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, Nikki Haley ta ba da Amurkawa mamaki bayan da kwatsam ta bayyana shirinta na yin murabus. Kodayake ta gaya ma Shugaba Trump tun watanni shida da su ka gabata.
Ga dukkan alamu, idan ba a kai zuciya nesa ba, za a shiga rudu a kasar kamaru sanadiyyar takaddamar bayan zaben Shugaban kasa. Wannan ko ya biyo bayan cewa da wani dan adawa ya yi shi ya ci zaben Shugaban kasa, duk kuwa da bai gabatar da hujja ba.
Babbar magana, wai dan sanda ya ga gawar soja. Wannan magana na nemar tabbata a jahar Filato, inda aka tura sojojin sama da ku,a jiragen yaki saboda ganin yadda rigimar da ake yi, ga dukkan alamu, ta fi karfin 'yansanda.
Kamar yadda akasarin masu hasashe su ka hango tun da farko, yanzu ta bayyana cewa za a buga ne tsakanin Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya, Atiku Abubakar, a zaben da akasarin masu lura da al'amura ke ganin za a yi ta - a kalla - a siyasance.
Kallo ya koma kasar Brazil, inda za a buga a zagaye na biyu tsakanin Haddad, mai ra'ayin sassauci da Jair, wanda ake ma lakabin Donald Trump din Brazil, saboda ra'ayin rikau dinsa.
Da alamar dai kasar Saudiyya da kasar Turkiyya za su saka wando guda, bayan da Turkiyya ta zargi Saudiyya da kashe dan jaridar Saudiyya mai gudun hijara a Amurka mai suna Jamal Khashoggi.
Yayin da masana'antun da ke amfani da na'urori masu haddasa zafi ke karuwa a duniya, Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa duniya za ta fuskanci bala'i mai tsanani matukar ba a rage dumamar ba.
A ziyarar kasashe hudu da uwargidar Shugaban Amurka Melaniya Trump ta ke yi, ta isa kasa ta hudu kuma ta karshe wato Masar, inda aka ma ta kyakyawar tarba, kamar yadda aka ma ta a kasashen Ghana da Malawi da kuma Kenya.
Bayan an shafe makwanni ana zafafan muhawarori da takaddama da kuma zarge-zarge kan cancanta ko rashin cancantar Brett Kavanaugh a matsayin alkali a Kotun Kolin Amurka, daga karshe dai, jiya Asabar Majalisar Dattawan Amurka ta amince da nadin nasa.
Uwargidar Shugaban Amurka Donald Trump, Melania Trump na gaba da kammala ziyarar kasashe hudu da ta kai Afirka, inda ta je makaranta da makebar dabbobin da ake tattalinsu da sauran wurare.
Da alamar yawan farautar dukiyar Afirka da 'yan China ke yi ba kakkautawa, na cigaba da janyo masu tsana daga wasu 'yan Afrika.
A wani cigaba ga tsirarun jinsi a fadin duniya, wata 'yar kabilar Yazidi da kuma wani bakar fata sun ci lambar yabo ta zaman lafiya ta Noble. Duk da ya ke ba wannan ne karon farko da tsirarun jinsi su ka ci wannan lambar yabo ta Nobel ba, wannan zai kara masu kwarin gwiwa.
Zamantakewar Jama'a
Domin Kari