Jihar Kano ta arewacin Nijeriya na nan na kan shirye-shiryen bukin cikar Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero shekaru 50 bisa gadon sarauta.
Mataimakin Shugaban bangaren Kungiyar Gwamnonin Nijeriya na zargin jam'iyyar PDP mai mulkin Nijeriya da yin katsalandan a zaben kungiyar na kwanan nan
Dokar Ta Baci Na Taimaka Wa Barayi A Jihar Adamawa
A yayin da ake shirin shagulgulan ranar dimokaradiyya a goba 29 ga watan Mayu, 'yan Nijeriya na ta bayyana ra'ayoyinsu game da halin da kasar ke ciki; ita kuma hukuma na ta bayani.
Mazauna jihohin Borno da Yobe da Adamawa da kuma kungiyoyi masu zaman kan su na cigaba da kokawa kan rashin sadarwa ta wayar selula da kuma zargin gallazawa.
Yanzu an tabbatar cewa iyayen Michael Adebolajo, daya daga cikin mutane biyun nan da su ka kashe wani sojan Burtaniya a birnin London, 'yan Nijeriya ne.
Ana kyautata zaton a kalla daya daga cikin mutane biyun nan da su ka kashe wani sojan Burtaniya a bisa titin London dan Nijeriya ne.
Wasu motoci shake da bama-bamai sun tarwatse a mashigar barikin soja a garin Agadez da garin Arlit, inda mutane 19 su ka mutu.
Kungiyar Wanzar da zaman lafiya ta matasan Musulmi ta na kan yada akidojin zaman lafiya bisa ga koyarwar addinin Musulunci tare kuma da taimakwa dalibai
Kwanaki biyar bayan da sojojin Nijeriya su ka fara kai farmaki kan 'yan Boko Haran a Arewacin kasar hukumar sojin kasar ta ce an kama 'yan kungiyar 65 aka kashe kuma 10.
Sojoji sun kafa dokar hana fita ta sa’o’i 24 a sassan birnin Maiduguri na arewa maso gabashin Nijeriya
Wasu mutane a Yola, hedikwatar jihar Adamawa, sun bayyana ra'ayoyinsu game da yadda dokar ta baci ke gudana a jihar da kuma yadda ta shafe su
Jam'iyyar PDP mai mulki a jihar Adamawa da Nijeriya ta ci zaben Majalisar Wakilai na cike gurbi da aka gudanar jiya Asabar a jihar Adamawa.
Kafafen yada labaran Nijeriya sun ce wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da mata, da diya da kuma direban wani alkalin kotun koli
Mata da wasu da abin ya shafa masu yawa ne dai su ka halarci taron yaki da cutar polio da Muryar Amurka ta shirya a birnin Maiduguri.
A wani taron da ta yi yau a babban birnin Tarayyar Nijeriya Abuja, jam'iyyar adawa ta CPC ta amince ta shiga sabuwar jam'iyyar hadaka ta APC.
Tsohon Shugaban Masar Hosni Mubarak ya sake gurfana a gaban wata kotu a birnin al-Khahira don sake fuskantar shari’a game zargin hannu a mace-macen daruruwan masu zanga-zanga a yayin boren zaburowar Larabawa na 2011.
Hukumomi a Somalia sun ce wani dan kunar bakin wake da mota, ya kai hari kan wata tawagar motoci a birnin Mogadishu
Jami’ai a Isira’ila sun ce Isira’ilar ta kai hari kan wasu kayan yakin da Syria ta yi niyyar kai ma ‘yan Hezbollah
Domin Kari