Jagoran Kungiyar IPOB mai neman ballewa a kudu maso gabashin Najeriya Nnamdi Kanu, da dan fafutukar kafa kasar Yarbawa a kudu maso yamma Sunday Igboho, sun shigar da karar gwamnatin Najeriya a gaban kotu, a yayin da gwamnatin ke kokarin hukunta su bisa zargin ta da zaune tsaye.