Gwamna Mohammed Jibrilla Bindow na jahar Adamawa ya samu sa'ida a kalla a halin yanzu, bayan da wata kotun tarayya da ke Birnin Tarayya, Abuja ta yi fatali da kararsa da aka yi cewa ya mallaki takardun kammala makaranta na bogi. Amma da zauran zance.
Duk da ya ke an gama da zaben shugaban kasar Najeriya, har yanzu fagen siyasar Najeriya na tsuma. Wannan kuwa ba zai rasa nasaba da muhimmancin da ake bai wa zaben gwamnonin jahohi ba. Tuni dai APC da PDP su ka fara karce kasa don shirin bugawa musamman a wasu jahohin.
Yayin da yakin neman zabe ke dada tsanani a Najeriya, an shiga yada labarai ko jita-jita da zummar yin illa ga abokan karawa. Watakila irin wannan al'amari ne ke neman girgiza jahar Sakkwato, inda aka ce wai kujerar Mai Alfarma za ta yi rawa.
A cigaba da hare-haren da Amurka ke kai wa kan mayakan kungiyoyi masu tsaurin ra'ayi a Afirka, ta kashe mayakan al-Shabab a kalla 35 a hari na baya bayan nan.
Yayin da ake cigaba da tattara sakamakon zaben Shugaban kasar Najeriya, zuwa yanzu Shugaba mai ci, Muhammadu Buhari, ya sha gaban Alhaji Atiku Abubakar, babban mai kalubalantarsa na babbar jam'iyyar adawa ta PDP.
Kamar yadda tun farko aka nuna fargabar zai faru, fada ya sake barkewa a Sudan Ta Kudu duk da yarjajjeniyar zaman lafiyar da aka cimma.
A wani al'amari mai tayar da hankali, wata babbar gobara ta kashe mutane da dama a Dhaka, babban birnin kasar Bangladesh baya ga mummunar barna da ta yi.
McCabe ya ce mai yiwuwa Trump ya aikata wani babban laifi, lokacin da ya kori Shugaban hukumar bincike ta FBI James Comey a watan Mayu na 2017, a lokacin Comey na jagorantar binciken alakar kwamitin yakin neman zaben Trump da kasar Rasha, game da zaben Shugaban kasar Amurka na 2016.
Ya kuma gargadi sojojin Venezuela cewa muddun su ka barar da wannan dama ta ahuwa, “ba za ku sami gabar fita ku hau tudun mun tsira ba; ba mafita gare ku, kuma ba abin yi gare ku.” Trump ya kara da cewa, “Za ku yi asarar komai.”
Yayin da kasar Somaliya ke gab da shiga sahun kasashe masu arzikin man fetur, gwamnatin kasar ta ce ta na shirin gayyatar kamfanonin hako man fetur su shigo a hada hannu a ci arziki
“Ban samu umurnin rage yawan sojojinmu da ke Afghanistan ba,” abin da Shanahan ya gaya ma manema labarai kenan, gabanin ziyarar ba-zata da ya kai birnin Kabul jiya Litini.
Fadar Shugaban Amurka ta White House da ‘yan majalisar dokokin na fuskantar cikar wa’adin ranar Jumma’a, lokacin da kudin tafi da gwamnati zai sake karewa ga rubu’in ma’aikatun gwamnati.
Masu kamfanin rukunin motocin jigilar majinyata na Aamin sun fada wa ‘yan jarida cewa sun dauko gawarwaki a kalla 9, ciki har da na wasu mata uku.
Trump zai yi jawabin ne mako guda bayan ranar 29 ga watan Janairu da ya kamata ya yi, wato lokacin da Pelosi ta taka mar birki da cewa jawabin bai yiwuwa har sai an kawo karshen rufe ma’aikatun gwamnatin.
Ya kara da cewa, “Yanzu haka, wannan binciken, a gani na, na dab da kammala, kuma ina fatan za mu samu rahoton daga Mueller ba tare da bata lokaci ba.”
“Matakin da aka dauka yau zai tabbatar da cewa daga yanzu ba za su iya wawushe dukiyar mutanen Venezuela ba,” inji Bolton.
A yau dinnan Litini Isira'ilar ta amsa cewa ita ta kai hare-hare kan wasu kayan yaki na Iran da ke cikin Siriya.
Wata kungiya mai alaka da al-Kaida ta yi ikirarin cewa, ita ta kai hari jiya Lahadi, kan wani sansanin sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD da ke arewacin Mali
Yau Litinin an shiga rana ta 31 da rufe wasu ma’aikatun gwamnatin Amurka, a yayin da kuma Shugaban Majalisar Dattawa, dan Republican, ke shirya yadda za a kada kuri’a, kan wata shawara da Shugaba Donald Trump ya gabatar ta a daidaita.
Duk da yake kotun shari'ar manyan laifuka ta kasa da kasa ta wanke tsohon Shugaban Ivory Coast Laurent Gbagbo daga zargin aikata laifin cin zarafin bil'adana, da sauran rina a kaba saboda masu gabatar da kara sun ce za su daukaka kara.
Domin Kari